NDC ta Kano ta warware sabani da Kwankwaso, Mairiga ya ci gaba da zama shugaba

IMG 20260506 WA0201 575x430

Shugaban Jam’iyyar NDC na Jihar Kano, Hussaini Isah Mairiga, ya ce jam’iyyar ta warware rikicinta na cikin gida biyo bayan wani taron da suka yi da shugaban kungiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A cewar shugaban, an gudanar da taron ne a ranar Talata a Abuja.

Mairiga ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da SolaceBase a ranar Laraba, inda ya ce shigowar shugabannin jam’iyyar ya taimaka wajen maido da hadin kai bayan tashin hankalin da ya barke a reshen jam’iyyar na Kano.

Rikicin, wanda yasa taron Abuja, ya samo asali ne sakamakon ficewar Kwankwaso daga jam’iyyar ADC bayan dogon rikici na cikin gida da ya ke nuna rashin tabbas din jam’iyyar gabanin babban zaben shekarar 2027.

Shigowarsa cikin NDC tare da tsarin siyasarsa ya haifar da damuwa a tsakanin shugabannin jam’iyyar a Kano.

Mairiga ya yi fargabar cewa tasirin Kwankwaso da kungiyar Kwankwasiyya na iya mamaye tsarin jam’iyyar a jihar, lamarin da zai iya sauke shugabannin da ake da su.

Lamarin ya haifar da tashin hankali a tsakanin mambobi, lamarin da ya sa shugabannin jam’iyya na kasa suka shiga tsakani, wanda ya kai ga gudanar da taron sulhu na Abuja.

Da yake bayani kan sakamakon taron, Mairiga ya ce bangarorin biyu sun amince da ajiye bambance-bambancensu domin hadin kai da nasar zabe.

“Ku sani rikici ya barke tsakanin mambobin NDC da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso bayan ya shigo jam’iyyar,” in ji shi, yana mai cewa rashin jituwar ya zama kalubale ga hadin kan jam’iyyar.

Ya kara da cewa bayan sun fahimci illar rikicin ne masu ruwa da tsaki suka nemi warware shi. “Daga baya muka fahimci cewa wannan rikici ba zai kai mu ga nasara ba,” in ji shi.

A cewarsa, shugabannin jam’iyyar na kasa ne suka shiga tsakani don sulhuntawa, lamarin da ya haifar da sakamako mai kyau.

Ya ce taron ya ba kowa dama ya bayyana damuwarsa tare da cimma fahimta daya.

“Shugabanninmu daga Abuja sun biyo mu, muka tafi muka warware dukkan matsalolinmu,” in ji Mairiga.

Da yake bayyana tsarin da ake da shi yanzu, ya ce Kwankwaso na ci gaba da zama shugaban kungiyar Kwankwasiyya, yayin da shi kuma ke ci gaba da zama shugaban NDC na Kano, tare da cewa bangarorin biyu sun amince da yin aiki tare.

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar a jihar sun amince da sabon tsarin kuma yanzu sun hada kai gabanin zaben.

Mairiga ya kuma bayyana cewa jam’iyyar na mara wa wata manufa ta siyasa guda baya, yana mai nuna kwarin gwiwa kan shirye-shiryensu.

“Yanzu dukkan mambobi na aiki tare domin tabbatar da nasara,” in ji shi, ya kara da cewa za su fara shirye-shirye cikin gaggawa da zarar ya koma Kano.

“Za mu fara cikakkun shirye-shirye domin tabbatar da nasarar Obi a matsayin shugaban kasa da Kwankwaso a matsayin mataimakin shugaban kasa,” in ji shi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here