Mambobin jam’iyyar PDP biyu sun sauya sheka zuwa APC

Reps Reps 750x430

Wasu ‘yan majalisar wakilai biyu sun sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Kakakin majalisar, Tajudeen Abbas ne ya sanar da sauya shekar su a cikin wata wasika da aka karanta a zauren majalisar a ranar Talata.

‘Yan majalisar dai sun haɗa da Adamu Tanko mai wakiltar Suleja, Gurara, da Tafa a jihar Neja, da Jallo Husseini Mohammed, mai wakiltar mazabar Igabi ta Kaduna, sun bayyana sauya shekar tasu ne a wata wasika da kakakin majalisar Dakta Tajudeen Abbas ya karanta a zauren majalisar.

Karanta: Kana zubar da ƙimar mahaifinku a Arewa – Adnan ga Seyi Tinubu

Da suke bayyana rarrabuwar kawuna a cikin jam’iyyar PDP a matsayin dalilinsu na sauya sheka jam’iyyar, masu sauya shekar sun kuma bayyana cewa akidunsu na siyasa a yanzu sun fi dacewa da na APC.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here