Shugaban kasa, Bola Tinubu ya rantsar da Dr Muttaqha Rabe Darma a matsain sabon ministan gidaje na kasar.
Dr Darma dan asalin jihar Katsina ya maye gurbin Ahmed Musa Dangiwa, wanda ya yi murabus a baya-bayan nan.
An rantsar da sabon ministan ne a wani kwarya-kwaryar biki da aka gudanar a fadar shugaban kasar da ke Abuja.
Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwarsa ga Dr Darma, saboda tarihin abubuwan da ya gabatar a baya.
Dr Darma babban malamin jami’a ne kuma gogaggen ma’aikacin gwamnati masani a bangaren ci gaba. Ya yi karatu a Jami’ar Bayero ta Kano da Jami’ar Benin da Jami’ar Liverpool da kuma Jami’ar Atlantic International inda yayi digirin shi na uku.
Darma ya rike mukamai da dama a jiharsa ta Katsina ciki har da kwamishinan ayyuka da sauransu.













































