Jerin Ministoci: Gbajabiamila Ya Magantu Kan Lokacin Da Za A Sake Tsammanin Rukuni Na Biyu.
Gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu na iya kirkiro sabbin ma’aikatu daga wadanda ake da su, Femi Gbajabiamila, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, ya bayyana a ranar Alhamis a Abuja.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa Gbajabiamila ne ya mika jerin sunayen ministocin ga majalisar dokokin kasar kuma shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ya karanta.
“Shugaban kasa yana da niyyar raba mukamai ko kuma sake fasalin ma’aikatun ta yadda za ku ji labarin sabbin ma’aikatun da ba ma’aikatu kadai ba a da.
Gbajabiamila ya ce an zabo wadanda aka nada ne bayan da shugaban ya ta tantance su.
Ya ce za a aika kashi na biyu mai kunshe da sunaye 13 ga majalisar, inda ya ce hakan na daga cikin tsarin samar da majalisar ministocin gwamnati.
‘’Kamar yadda kuka sani yana da kwanaki 60 daga lokacin rantsar da shi, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada. Ya cika wannan bukata ta kundin tsarin mulki ta hanyar gabatar da sunaye 28 a yau.
‘’Kamar yadda wasikar tasa ta bayyana, kuma aka karanta a zauren majalisar, sauran sunayen, ba a tabbatar da adadin su nawa ba ne, mai yiwuwa kusan 12, watakila 13, za a mika wa majalisar a kwanaki masu zuwa.














































