Shugaban Hukumar Karbar Korafe-Korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Saidu Yahaya, ya ajiye aikinsa.
SolaceBase ta rawaito cewa Yahaya ya mika takardar murabus dinsa a ranar Talata.
Read also: Da Kwankwaso ne a wajen rantsar da Tinubu ba za a yi masa abin da a ka yi wa Ganduje ba — Danzago
Murabus din nasa ya biyo bayan matsin lamba daga Gwamnatin Jihar Kano kan abin da ake zargin gazawarsa wajen sauke nauyin da ake tsammani daga gare shi.
Read also: Fitaccen malamin addinin musuluncin man Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu
An nada shi shugaban PCACC a watan Agustan 2025, bayan karewar wa’adin tsohon shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimin Gado.
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da nadin nasa na shekaru biyar.
Idan za a iya tunawa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya soki shugaban a bainar jama’a a kwanakin baya kan abin da ya bayyana a matsayin rashin nuna kwazo a matsayinsa na shugaban hukumar yaki da cin hanci.
Ana sa ran Sakataren Shari’a na hukumar, Hafsat Kutama, za ta karbi ragamar shugabancin hukumar a matsayin mukaddashiya daga yau Laraba.












































