Wani jirgin saman horar da sojojin saman Najeriya FT-7NI ya yi hatsari a Makurdi, babban birnin jihar Benue.
Daraktan hulda da jama’a da labarai na rundunar NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a. Ya ce matukan jirgin biyu da ke cikin jirgin sun tsira kuma ana kan kula da su a wani asibitin sojoji. Gabkwet ya ce:
“An yi sa’a matukan jirgin biyu sun tsira a hatsarin bayan da suka yi nasarar fita daga jirgin. Bugu da kari, ba a rasa rai ko daya, ko lalata kaya a yankin da abun ya faru ba. ”
“Yanzu haka dukka matukan jirgin na karkashin kulawa a asibitin sojoji, Makurdi. A halin da ake ciki, shugaban hafsan soji, Air Vice Marshal Hasan Abubakar, ya kafa wani kwamitin bincike don gano abun da ya haddasa hatsarin.”













































