Tinubu ya nada Ganduje, Gawuna, Afikuyomi da wasu 42 a mukaman hukumomin gwamnati

Bola Tinubu sabo 720x430

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin shugabannin kwamitoci da manyan daraktoci a hukumomi 42 na tarayya, tare da sakataren Hukumar Kare Farar Hula, Shige da Fice, da Gidajen Yari.

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman kan bayanai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, an bayyana cewa nadin ya fara aiki nan take.

Daga cikin wadanda aka nada sun hada da Abdullahi Ganduje a matsayin Shugaban Hukumar Filayen Jiragen Sama (FAAN), Nasiru Gawuna a matsayin Shugaban Bankin Lamunin Gidaje na Tarayya, da Tokunbo Afikuyomi a Hukumar Kula da Fasaha (NOTAP).

Ga wasu daga cikin sunayen:

Ganduje: Shugaban FAAN

Gawuna: Shugaban Federal Mortgage Bank

Tokunbo Afikuyomi: Shugaban NOTAP

Kayode Opeifa: MD na Nigerian Railway Corporation

Magnus Abe: Shugaban NA Great Green Wall

Shugaban ya gargadi shugabannin da kada su tsoma baki cikin ayyukan gudanarwa domin mukamansu ba na aiwatarwa ba ne.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here