Tawagar gwamnatin tarayya ta isa kasar Saudiyya domin karbar gawar marigayi hamshakin dan kasuwa kuma dattijon Najeriya Alhaji Aminu Dantata, gabanin binne shi a birnin Madinah mai alfarma.
Jaridar SolaceBase ta ruwaito cewa Alhaji Dantata ya rasu ne a birnin Abu Dhabi na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Asabar, yana da shekaru 94 a duniya.
Wata sanarwa da mataimaki na musamman ga ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Litinin, ta ce tawagar da ta bar Najeriya da yammacin ranar Lahadi, ta isa Madina da sanyin safiyar Litinin.












































