Sojin Isra’ila sun bayyana cewa suna gwabza kazamin fada a kudancin Gaza

c2de6150 3703 44cc ab77 1f9207a12424
c2de6150 3703 44cc ab77 1f9207a12424

Rundunar sojin Isra’ila tace dakarunta  na ruwa da na sama sun kai hari kan wasu wurare a yankin Zirin Gaza inda suke gwabza kazamin fada.

Tace sojojinta a birnin Gaza sun kashe gomman ƴan ta’adda a musayar wuta daban-daban cikin sa’o’i 24 da suka wuce.

Sojojin sun kuma lalata wasu gine-gine guda biyu wadanda Hamas ke amfani da su a birnin Beit Lahiya da ke arewacin Gaza.

Karanta wannan: BCPG ta bukaci Tinubu da ya dakatar da shirin kara farashin siminti a 2024

Wannan na zuwa ne yayin da Falasdinawa ke cewa tankokin yakin Isra’ila na ci gaba da lugudan wuta a Gaza har cikin dare.

Ma’aikatar lafiya karkashin ikon Hamas a Gaza ta ce an kashe mutum 187 a wasu hare-hare cikin sa’o’i 24 da suka wuce.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here