Rikicin Natasha da Akpabio – ya kamata a yi bincike a fili domin ceto majalisar dattawa – Bukola Saraki

Bukola speaks

Tsohon shugaban majalisar dattawa kuma Wazirin masarautar Ilorin, Dakta Abubakar Bukola Saraki, ya yi kira da a gudanar da bincike a fili kan zarge-zarge da cin zarafi da kuma rashin mutunta dokokin majalisar dattawa da ke faruwa tsakanin shugaban majalisar fattawa, Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Saraki, wanda ya kasance shugaban majalisar dattawa ta 8 tsakanin 2015 -2019, ya bayyana cewa binciken ya zama dole domin gano gaskiya da kuma kare mutuncin majalisar a matsayin ta na hukuma.

Karin karatu: Akpabio ya so ya kwanta da ni kafin ya bar ni in gabatar da ƙudiri – Natasha

A wani dogon rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar da yamma, tsohon gwamnan jihar Kwara kuma jigo a jam’iyyar adawa ta PDP, ya bukaci majalisar dattawa ta 10 ta gabatar da Akpabio da Natasha don gudanar da bincike na gaskiya domin a gano tushen lamarin, inda ya kara da cewa irin wannan lamari ya taba faruwa lokacin da yake shugaban majalisar dattawa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here