Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi hasashen cewa za’a sami rana da kura daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar.
NiMet ta fitar da wannan sanarwar ne a ranar Lahadin da ta gabata a Abuja cewa za a samu kura a ranar Litinin a yankin arewacin kasar nan.












































