Gwamnatin tarayya ta aikewa gwamnonin jihohinta tirelolin shinkafa 20

Shinkafa, Gwamnatin, tarayya, aikewa, gwamnonin, jihohinta, tirelolin
Gwamnatin tarayyar Najeriya tace ta bawa kowacce jiha a Najeriya ciki harda babban birnin tarayyar Abuja tirelar shinkafa 20 domin rabawa talakawa...

Gwamnatin tarayyar Najeriya tace ta bawa kowacce jiha a Najeriya ciki harda babban birnin tarayyar Abuja tirelar shinkafa 20 domin rabawa talakawa.

Ministan yada labarai, Mohamed Idris, ne ya bayyana hakan bayan kammala taron majalisar zartaswa a ranar Litinin.

Karin labari: Kotu ta kori Dan Majalisar Wakilai a Sokoto

Ya ce kowace tirela tana ɗauke da buhun shinkafa 1,200 mai nauyin kg25 da aka ba gwamnonin jihohi a wani mataki na ragewa talakawa raɗaɗin ƙarancin abinci da tsada da ake fuskanta a ƙasar.

Haka kuma, gwamnatin tarayyar ta ce tana fatan gwamnonin jihohin za su raba kayan abincin ga mabuƙata a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.
Ana dai fama da tsadar kayan abinci da ake danganta al’amarin da matsalolin tattalin arziki wanda janye tallafin mai da matsalar tsaro suka haddasa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here