Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a jihar biyo bayan zanga-zanga da barnata dukiyoyi da ke da alaka da mutuwar wasu da ake zargin masu hakar ma’adanai ne ba bisa ka’ida ba a hannun Hukumar Tsaro ta Civil Defence.
Bago ya sanar da dokar hana fitar ne a yayin wani taron manema labarai a ranar Juma’a, yana mai cewa za ta fara aiki nan take bayan sallar Juma’a.
Read also: Majalisa ba ta janye batun kudurin dokar gyaran haraji ba – Akpabio
Ya ce matakin ya zama dole don dawo da kwanciyar hankali bayan da masu zanga-zangar suka lalata dukiyoyin gwamnati, banki, ofisoshin jam’iyyun siyasa da kuma shagunan ‘yan kasuwa masu zaman kansu.
“Daga zarar an idar da sallar Juma’a, mun sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a nan,” in ji Bago.
“Kamfanin Sufuri na Jiha, duk motocin bas da muke da su a can an lalata su. An kai hari Bankin Sterling. An lalata ofisoshin jam’iyya, an lalata kasuwancin jama’a,” in ji shi.
Gwamnan ya ce tashin hankalin ya sa ‘yan daba sun mamaye tituna, hakan ya sa ya zama wajibi gwamnati ta sanya takunkumi don hana ci gaba da aikata barna.
“‘Yan daba sun mamaye tituna, kuma akwai bukatar mu dakile wannan abu domin mu samu natsuwa a cikin al’ummaku,” in ji shi.
Bago ya yi kira ga mazauna jihar da su ci gaba da kasancewa cikin natsuwa da kuma yin hakuri yayin da hukumomi ke aiki don dawo da doka da oda.
Read also: Tinubu Ya Umarci Jami’an DSS Da Su Bar Ofishin EFCC Cikin Gaggawa
“Muna kira ga al’ummar jihar Neja, don Allah ku kasance masu juriya da hakuri,” in ji shi.
Dokar hana fitar ta biyo bayan zanga-zanga a wasu sassan Jihar Neja bayan mutuwar wasu da ake zargin masu hakar ma’adanai ne ba bisa ka’ida ba da Civil Defence ta tsare.
Gwamnan Jihar Neja ya tabbatar a baya cewa mutane 37 da ake zargin masu hakar ma’adanai ne ba bisa ka’ida ba sun mutu a hannun hukumar, inda ake gudanar da binciken kwakwaf, gwajin lafiya domin gano musabbabin mutuwar.
An kama wadanda ake zargin masu hakar ma’adanai ne ba bisa ka’ida ba a yayin samamen yaki da ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a yankin Wushishi/Lukoto na jihar a ranakun 15 da 16 ga Satumba.
Daga bisani hukumar ta kafa kwamitin bincike domin bincikar yanayin da ya kai ga mutuwar tasu, ciki har da yanayin da suke a lokacin da aka kama su, tsawon lokacin da suka yi a tsare, yanayin tsarewa da kuma kulawar lafiya da aka ba su.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya kuma dakatar da kwamandan rudunar tsaron ta Civil Defence na Jihar Neja, Suberu Siyaka Aniviye, tare da bayar da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Read also: INEC ta ɗebe kayan zabe masu muhimmacin daga ofishinta na Imo
Gwamnatin Tarayya, ta hannun Ministan yada labarai da wayar da kai, Mohammed Idris, ta ce ba za a yi wani yunkuri na kare duk wanda aka samu da laifi ba, yayin da ta yi gargadi game da yanke hukunci kafin kammala binciken.
Har zuwa yanzu ba a tabbatar da musabbabin mutuwar ta su ba.











































