Dan Majalisar Wakilai, Bello El-Rufai, ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyr ADC na kujerar karamar hukumar Kaduna ta Arewa ba tare da wani hamayya ba.
A cikin wata sanarwa a ranar Asabar, Bello, da Ga tsohon gwamna Nasir El-Rufai, ya ce ya samu kuri’u 7,727 a zaben fidda gwani na ADC na kujerar tarayya.
Dan majalisar ya gode wa shugabannin ADC da mambobinta bisa “bayyana amincewa da dogaro da shi ba tare da tangarda ba”.
“Alhamdulillah, na yi matukar alfahari da tawali’u kan fito dani ba tare da hamayya ba a matsayin dan takarar tutar jam’iyyar ADC na karamar hukumar Kaduna ta Arewa a zaben fidda gwani da aka kammala, da jimillar kuri’u 7,727,” el-Rufai ya ce.
“Ina godiya ta musamman ga shugabancin jam’iyya, wakilai, masu ruwa da tsaki, magoya baya, da al’ummar Kaduna ta Arewa bisa wannan nuna amincewa da dogaro da ni ba tare da tangarda ba.
“Na yi aiki tukuru tsawon shekaru uku tare da tawagata.”











































