Dalibin Kano ya zama Zakara a gasar kacici-kacicin Computer ta Kasa

IMG 20220723 WA0154
IMG 20220723 WA0154

Dan asalin jihar Kano, Abdul Yassar Yahaya Musa ya zama daya daga cikin ’yan takara hudu da suka lashe gasar kacici-kacici ta kasa ta a darasin Kwamfuta ta shekara-shekara.

Sakataren kungiyar Nigerian Computer Society reshen jihar Kano, Malam Lukman Bayero, shi ne ya shaida wa jaridar Solacebase a ranar Asabar cewa dalibai biyu daga makarantun sakandare 35 da ke Kano suka halarci gasar kacici-kacicin.

“Wannan shi ne karon farko da muka samu wanda ya yi nasara a gasar da aka fara sama da shekaru ashirin da suka wuce,” in ji Bayero.

”Rijistar gasar ana bude ta ne a watan Maris kuma ana iya shiga ta adireshin Internet wato www.ncs.org.ng”
Jaridar Solacebase ta Turanci ta cika shekaru biyar

Ya kuma bayyana cewa duk mutane hudun da suka yi nasara za a basu lambar yabo a ranar 2 ga watan Agustan shekarar nan da muke ciki ta 2022 a Abeokuta dake jihar Ogun.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here