DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin tarayyar ta dakatar da ƙarin harajin kiran waya

Dr Isa Ali Pantami
Dr Isa Ali Pantami

Gwamnatin tarayyar ta dakatar da shirin ƙarin harajin kiran waya sadarwa.

Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki a Fasahar Zamani, Isa Pantami ne ya sanar da dakatarwar a yau Litinin yayin taron kaddamar da kwamitin shugaban kasa haraji kan hanyoyin sadarwa don bunƙasa ɓangaren tattalin arziki ta hanyar fasahar zamani a Abuja.

Ministan ya ce tun tuni fannin sadarwa ya cika da harajai da yawa.

Gwamnatin tarayya ta hannun ofishin kasafin kudi na tarayya a baya ta bayyana cewa za ta fara aiwatar da shirin fitar da kudaden da ta ke bukata a kan harkokin sadarwa da abubuwan sha a shekarar 2023.

Sai dai Pantami ya ci gaba da cewa ba ya goyon bayan aiwatar da wannan harajin da zai kara tsadar harkokin sadarwa ga ‘yan Najeriya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here