An kashe mutum 25 a wani hari a jihar Borno

Nigeria Kidnappings Bandits deputy 768x528 1
Nigeria Kidnappings Bandits deputy 768x528 1

Rundunar ‘yan sandan Najeriya sun ce akalla mutum 25 ne aka kashe a wani hari da masu iƙirarin jihadi suka kai jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

An kai harin ne a garin Dikwa wanda ke kusa da garuruwan da ‘yan ta-da-ƙayar-baya na Boko Haram ke da karfi.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tun 2009, hare-haren kungiyoyi masu tsassaurar ra’ayi ya kashe mutane sama da 350, 000 da ɗaiɗaita miliyoyi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here