Wakilin Jihar Sakkwato, Nura Abdullahi da ta Jihar Yobe, Aishatu Abdulmutallib sun yi nasarar lashe gasar karatun Alkur’ani ta kasa karo na 37 da aka gudanar a birnjn Gusau na Jihar Zamfara.
Rahotanni sun ce wanda ya yi nasara a bangaren maza Nura Abdullahi ya samu kambun gwarzon shekara ta Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar.
Hakazalika, Aishatu Abdulmutallib ta bangaren mata ta samu lambar yabo ta jarumar bana da uwargidan gwamnan jihar Zamfara, Hajiya Aisha Mattawalle a wajen bikin rufe gasar da aka yi a Gusau ranar Asabar.
Da yake bayyana sakamakon, shugaban kwamitin Farfesa Yalwa ya ce
Jarumin ajin maza Abdullahi ya samu nasara da maki 97.9 sai Abdullahi Sadiqu-Sadiq daga jihar Zamfara da maki 96.9 a matsayi na biyu sai Salish Abdullahi na jihar Niger da maki 95.9.
Muhammed Kabir na Kebbi ya zo na hudu da maki 94.7, Faruk Kabir na jihar Kano ya zo na biyar da maki 94.0 Usmanu Abubakar ya zo na shida a gasar.
Shugaban ya kuma bayyana sakamakon ajin mata kamar haka;
Aisha Abdulmutallib ta Yobe da maki 96.4 da Maimuna Hussaini daga FCT da maki 94.1.
Haka kuma Aisha Kabir ta jihar Gombe ta zo matsayi na uku da maki 93.5 sai kuma Zainab Habib ta jihar Kano a matsayi na hudu da maki 92.9.
Sauran sun hada da: Fatima Mustapha daga jihar Kaduna ta zo ta biyar da maki 92.5, yayin da ta shida Fatima Ahmad ta jihar Nasarawa da maki 92.3.
A nasa jawabin shugaban taron kuma Sarkin Wase a Jihar Nasarawa, Alhaji Jibirin Bala ya yi kira ga mahalarta taron da su yi amfani da lokacinsu wajen karantarwa da haddar Alkur’ani mai girma.
“Hakazalika ina so in yi amfani da wannan dama domin jajanta wa jihar da kuma iyalan duk wadanda suka rasa rayukansu ko kuma suka samu raunuka sakamakon hare-hare daban-daban da ‘yan bindiga suka kai a jihar,” in ji shi.
Da yake sanar da rufe gasar, Gwamna Bello Matawalle na Zamfara ya ce akwai bukatar matasa a jihar da ma kasar baki daya su jajirce wajen nazarin Littafi Mai Tsarki.
Matawalle ya ce dukkan wadanda suka halarci gasar sun yi nasara saboda Allah ya saka musu.
Ya roki wadanda suka yi rashin nasara da su kara himma don samun damammaki a nan gaba kuma wadanda suka yi nasara da su ninka kokarinsu don kammalawa a matakin kasa da kasa.













































