INEC ta tsayar da ranar 26 ga watan Fabrairu domin gudanar da zaben cike gurbi a jihohi 4 

INEC Mahmood
INEC Mahmood

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanya ranar 26 ga watan Fabrairu a matsayin ranar gudanar da zabukan cike gurbi na mazabu shida a jihohi hudu na kasar nan.

Hukumar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Mista Festus Okoye, kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a ya fitar a yammacin ranar Juma’a a Abuja.

Okoye ya ce an yanke wannan shawarar ne a taron mako-mako na INEC da aka gudanar a ranar Alhamis da kuma wani taro na musamman na ranar Juma’a, inda aka tattauna kan batutuwan da suka shafi zabukan da kuma sauya jadawalin wasu zabuka da kuma matsalar tsaro a wasu jihohin.

Okoye ya ce matakin ya biyo bayan bayyana guraben mukaman da kakakin majalisar wakilai da wasu shugabannin majalisun jihohi suka yi.

Kujerun a cewar OKoye sun hada da mazabar tarayya ta Akure North/Akure South, jihar Ondo; Jos North/Bassa, Plateau da Pankshin South State , Plateau.

Sauran sun hada da mazabar tarayya ta Ogoja/Yala, Cross River, Akpabuyo, Cross River da kuma Ngor-Okpala a jihar Imo.

Okoye ya ce za a gudanar da zaben fidda gwani ne a ranar 26 ga watan Fabrairu nan da nan bayan kammala zaben kananan hukumomin babban birnin tarayya.

Kwamishinan na kasa ya ce wasu daga cikin guraben sun taso ne sakamakon mutuwar mutanen da aka zaba, wanda hakan ya zama gagarumin cikas ga tsarin zabe da cika sharuddan tsarin mulki da na shari’a a cikin tsarin zabe.

Ya ce INEC ta yanke shawarar hada zaben mazabar jihar Ekiti ta gabas 1 da zaben gwamna a Ekiti wanda zai gudana a ranar 18 ga watan Yuni

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here