Tsohon Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Sani Lawan Kofar Mata, ya rasu.
Majiyoyi masu inganci sun shaida wa SolaceBase cewa Kofar Mata ya rasu ne a yammacin Lahadi a Kano sakamakon rashin lafiya.
Read also: Hukumar NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 129 dake gararamba a Jimhuriyar Nijar
Read also: Ƙungiyar Direbobin Tankar Mai ta buƙaci direbobi su yi watsi da sanarwar yajin aikin NUPENG
Marigayi dan siyasan abokin Malam Ibrahim Shekarau ne a jam’iyyar ANPP kuma ya shahara sosai a lokacin zaben gwamna na 2007.
Read also: Kano: Ƴan sanda sun kama mutane 9 bayan harin da jama’a suka kai ofishin ƴan sanda
Daga baya marigayin ya bar ANPP a 2011 tare da sauran manyan mambobin jam’iyyar kafin daga bisani ya koma jam’iyyar ACN.
SolaceBase ta tabbatar cewa za a gudanar da sallar jana’izarsa a gobe Litinin da misalin karfe 9.00 na safe a gidansa.












































