Tinubu Ya Rabawa Sababbin Ministocin Sa Mai’akatu

President Bola Tinubu signs
President Bola Tinubu signs

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya nada tsohon Gwamnan Jihar Jigawa a matsayin sabon Ministan Tsaro na Najeriya.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata takarda daga Fadar Shugaban Kasar ranar Laraba da ke dauke da jerin ma’aikatun da shugaban ya ba Ministoci 45 din da Majalisar Dattijai ta sahale masa ya nada.

Shugaban ya kuma nada Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike a matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, yayin da tsohon Gwamnan Filato, Simon Lalong ya zama Ministan Kwadago.

Ita kuwa Mariya Bunkure ta zama Ministar a Ma’aikatar Babban Birnin Tarayya, sai Atiku Bagudu da ya zama Ministan Kasafi da Tattalin Arziki.

Yusuf Sununu – Ilimi

Nyesom Wike – Abuja

Mohammed Badaru – Tsaro

Ahmed Dangiwa – Gidaje da Raya Birane

Simon Lalong – Kwadago da Ayyuka

Bosun Tuani – Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani

Ishak Salaco – Karamin Ministan Muhalli

Wale Edun – Kudi da Tattalin Arziki

Bunmi Tunji – Ruwa

Adedayo Adelabu – Lantarki

Tunde Alausa – Karamin Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a

Dele Alake – Ma’adinai

Lola Ade-John- Yawon Bude Ido

Adegboyega Oyetola – Sufuri

Doris Anite – Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari

Uche Nnaji – Kimiyya da Fasaha

Nkiruka Onyejeocha – Karamar Ministar Kwadago da Samar da Ayyukan Yi.

Uju Kennedy – Ministar Mata

David Umahi – Ayyuka

Festus Keyamo – Sufurin Jiragen Sama

Abubakar Momoh – Matasa

Betta Edu – Walwala da Yaki da Talauci

Ekperikpe Ekpo – Karamin Ministan Iskar Gas

Heineken Lokpobiri – Karamin Ministan Man Fetur

John Enoh – Wasanni

Majiyoyi daga Fadar Shugaban Kasa dai sun ce ba a kai ga sanya ranar rantsar da sababbin Ministocin ba, amma kwanan nan ake sa ran fara yi musu bita.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here