Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya nemi Majalisar Dattijai ta tabbatar da sunayen mutane biyu domin a nada su a matsayin kwamishinoni a Hukumar Kula da Lantarki ta Najeriya (NERC).
Bukatar ta fito ne a cikin wata wasika da shugaban ƙasa ya aikawa Majalisar Dattijai, wanda shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta yayin zaman ta ko ranar Talata.
Tinubu ya bayyana cewa nadin an yi shi ne bisa sashe na 35 (1) da (3) na Dokar Lantarki ta 2023, wadda ke ba shugaban ƙasa damar nada kwamishinoni a hukumar kula da lantarki, tare da samun amincewar Majalisa.
Shugaban ƙasa ya ƙara da cewa nadin an yi shi ne don ƙarfafa hukumar yayin da take ci gaba da kula da sauye-sauyen da ake yi a kasuwar lantarki ta Najeriya.
Karanta: Majalisar Dattawa ta amince da bukatar Tinubu na tura sojoji zuwa Jamhuriyar Benin
Mutanen da aka nada sun haɗa da Aisha Mahmoud Kanti-Bello, wadda za a sake nadinta a matsayin kwamishina, da Fouad Animashaun, wanda aka nada a matsayin sabon kwamishina.
Tinubu ya lura cewa nadin su zai maye gurbin wani nadin da aka gabatar wa Majalisa a ranar 6 ga Agusta, 2025.
Ana sa ran Majalisar Dattijai za ta gudanar da bincike da tantance waɗannan sunaye a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa.













































