Sabbin jerin matsayi na hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA da aka fitar ranar Litinin, sun nuna cewa tawagar kwallon kafa ta Najeriya za ta kammala shekarar 2025 a matsayi na 38 a duniya.
Matsayin Najeriya bai canza ba idan aka kwatanta da jerin da aka fitar a watan Nuwamba, bayan da tawagar ta samu ci gaba da hawa matakai uku daga matsayi na 41 a baya.
A matakin Afirka, tawagar kwallon kafa ta Najeriya ta ci gaba da riƙe matsayi na shida, lamarin da ya nuna daidaiton matsayinta a nahiyar duk da canje-canjen da aka samu a duniya.
Gaba ɗaya, shekarar 2025 ta kasance mai gauraye ga Najeriya, amma tawagar ta kammala shekarar a matsayi 6 sama da inda ta fara a farkon shekarar, inda ta shiga shekarar ne a matsayi na 44.
Jerin farko na shekarar da aka fitar a watan Afrilu ya ɗaga Najeriya zuwa matsayi na 43, kafin daga bisani ta koma matsayi na 44 a watan Yuli da na 45 a watan Satumba.
Watan Oktoba ya kawo sauyi mai kyau, inda Najeriya ta haura zuwa matsayi na 41 bayan samun lambar azurfa a gasar cin kofin nahiyar Afirka AFCON, abin da ya zama mafi girman ci gabanta tun farkon shekarar 2024.
A matakin Afirka, ƙasar Maroko ce ke jagoranci da matsayi na 11 a duniya, sai Senegal a matsayi na 19, yayin da Aljeriya ta haura zuwa matsayi na 34, Masar kuma ta koma matsayi na 35, inda ta zama ta biyar a Afirka.
NAN













































