Majalisar dattawa ta amince da mutanen da Buhari ya nada a matsayin kwamishinonin NERC da NPC

BD08C13A 051B 40DD 8EF1 FEADD050DBA2
BD08C13A 051B 40DD 8EF1 FEADD050DBA2

Majalisar dattawa ta tabbatar da sunayen mutanen da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada a matsayin kwamishinonin hukumar kula da wutar lantarki ta kasa NERC da kuma hukumar kidaya ta kasa NPC.

Tabbatar da sunayen mutane hudu na NERC a ranar Laraba a zauren majalisar ya biyo bayan nazari tare da amincewa da kwamitin majalisar dattawan kan harkokin wutar lantarki ya yi.

Shugaban kwamitin Sanata Gabriel Suswam (PDP-Benue) ne ya gabatar da rahoton.

Wadanda aka tabbatar da su a matsayin Kwamishinonin NERC na kasa sun hada da: Dokta Yusuf O. Alli (Arewa Ta Tsakiya), Mista Chidi Ike (Kudu maso Gabas), Mista Nathan Rogers Shatti (Arewa maso Gabas) da Mista Dafe N Akpeneye (Kudu maso Kudu).

Majalisar dattawa ta kuma tabbatar da nadin mutane biyar da Buhari ya nada a matsayin kwamishinonin hukumar kidaya ta kasa (NPC).

Tabbatar da nasu ya biyo bayan yin la’akari da amincewa da rahoton kwamitin tantance mutane ya gabatar.

Shugaban kwamitin Sanata Ya’u Sahabi (APC-Zamfara) ne ya gabatar da rahoton.


Wadanda aka tabbatar da su a matsayin kwamishinonin NPC sun hada da: Cif Benedict Ukpong Effiong (Akwa-Ibom), Mrs Gloria Fateya Izonfo (Bayelsa), Mr Kupuchi Patricia Ori Iyanya (Benue), Dr Haluru Bala (Kebbi) da Dr.Eyitayo Oyekunle Oyetunji (Oyo). .

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here