Rev. Fr. Joseph Shekari, limamin cocin Katolika na St Monica’s, Ikulu Pari, wanda aka yi garkuwa da shi ranar Lahadi, wanda suka yi garkuwa da shi sun sako shi.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban darikar Katolika ta Kafanchan a jihar Kaduna , Rev. Fr. Emmanuel Okolo ya fitar.
Ya ce an saki Shekari da misalin karfe 10.30 na daren ranar Litinin.
Okolo ya godewa duk wanda ya yi addu’ar neman a sako limamin din, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan mai dafa masa abincin da aka kashe yayin harin.
Ya umurci dukkan limaman cocin da su gudanar da taron godiya ga Allah da ya gaggauta sakin Shekari tare da yi wa mamaci addu’o’in girkinsa da ya rasu.













































