Kotu ta sake umartar EFCC da ta saki Emefiele

Emefiele, EFCC, hukuma, bankado, zargi
Hukumar EFCC ta sake bunciko shari’ar da ake yi wa tsohon Gwamnan CBN Godwin Emefiele da aka dakatar bisa tuhumar sa da zamba a wata babbar kotu da ke Abuja...

Mai shari’a Olukayode Adeniyi na wata babbar kotun birnin tarayya ta sake umar tar hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) da ta saki tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN).

Mai shari’a Adeniyi ya ba da umarnin farko ne a ranar Juma’a bayan sauraron karar da aka shigar a gaban kotu, a hannun dama mai lamba M/122/2023 a cikin wata takardar sanarwa mai lamba FCT/HC/CV/040/2023, wanda Emefiele ya shigar.

Sai dai kuma abin takaicin shi ne, EFCC ta kasa bin umarnin a zaman da aka ci gaba da yi a ranar Litinin kamar yadda lauyan EFCC, Farouk Abdullahi ya shaida wa kotun cewa ba a fahimci umarnin ba.

Lauyan Emefiele, Matthew Burkaa, SAN, ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa ya shafe kwanaki 149 a tsare a hannun gwamnatin tarayya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here