Jerin Sunaye: Gwamnatin Tarayya ta bayyana sunayen jami’an NSCDC 21 da aka dakatar kan mutuwar masu hakar ma’adanai, ta kafa kwamitin bincike

NSCDC Minister

Gwamnatin Tarayya ta bayyana sunayen jami’an hukumar tsaron Civil Defence (NSCDC) 21 da aka dakatar kan mutuwar mutane 37 da ake zargin masu hakar ma’adanai ne ba bisa ka’ida ba a hannun hukumar a Jihar Neja.

An dakatar da jami’an har sai an kammala bincike mai zaman kansa kan mutuwar da ta faru a ranar Alhamis, 17 ga Satumban 2026.

Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ce ta sanar da dakatarwar a cikin wata sanarwa da minister ya sanya wa hannu a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce dakatarwar ta biyo bayan kafa kwamitin bincike mai zaman kansa mai mambobi 10 don bincikar lamarin.

Kwamitin zai kasance karkashin jagorancin Jonathan Kure, tsohon Mataimakin Darakta-Janar na Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), yayin da Farfesa Isa Hayatu Chiroma (SAN), tsohon Darakta Janar na Makarantar Koyon Shari’a ta Najeriya, zai zama sakatare.

Sauran mambobin sun hada da AIG mai ritaya Hosea Hassan Karma, Farfesa Olayinka Buhari, Farfesar Histopathology tsohon Babban Daraktan Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin, wakilin Majalisar Masarautar Minna da wakilin Gwamnatin Jihar Neja.

Kwamitin ya kuma hada da Alhaji Liman Sulaiman, Sakataren Kasa na Kungiyar Masu Hakar Ma’adanai ta Najeriya, lauya kuma mai fafutukar kare hakkin dan Adam Deji Adeyanju, Mrs Zainab Suleiman Okino ta Jaridar Blueprint da Dr George Agbakahi, manazarci kan harkokin jama’a.

An bai wa kwamitin makonni biyu don kammala aikinsa tare da gabatar da rahotonsa ga ministan.

A cewar sanarwar, ana sa ran kwamitin zai gano sahihan mutanen da suka mutu tare da bincikar kamasu, tsare su da kuma musabbabi da yanayin mutuwarsu.

Ministan ya kuma umurci kwamitin da ya gano alhaki, ciki, sakaci da kuma mummunan aiki, tare da bayar da shawarar matakin da ya dace da kuma diyya inda ta dace.

An dakatar da Kwamandan NSCDC na Jihar Neja, Suberu Aniviye, a baya.

Sauran jami’an NSCDC 20 da aka dakatar sune:

O/C Station Guard, SC Usman Isah Ndamaka

Station Guard, ASCI Hassan Mohammed

Station Guard, CCA Bala Mohammed

Jami’in Kame/O/C Bincike, CSC Oluwadare Sunday

Jami’in Kame, DCC Obafemi Elvis

Jami’in Kame, CSC Annas Shitto Lamino

HOD INT/INV, DCC Philip Ajayi

O/C Legal, ACC Barr. Stephen Tsado

Jami’in Aikin Dare, ASCI Alhassan Mohammed

Jami’in Tsaro, IC Abdullahi Sale

Jami’in Tsaro, IC Mohammed Sonfada

Jami’in Tsaro, CAI Liman Abubakar

Jami’in Tsaro, CAI Bala Usman

Jami’in Tsaro, IC Mohammed Jiya

Jami’in Tsaro, DSC Isah Suleiman

Jami’in Tsaro, CAI Ahmed Wushishi

Jami’in Tsaro, IC Sale Adamu

Jami’in Tsaro, IC Haruna Mohammed

Jami’in Tsaro, ASCI Aliyu Sallah

Jami’in Tsaro, CAI Isah Sanusi

Ministan ya mika ta’aziyya ga iyalan mamatan tare da yin kira da a kwantar da hankali yayin da ake ci gaba da bincike.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here