
Jami’an tsaro a Jihar Filato sun cafke mutanen da ake zargi sun kitsa kashe-kashen kwanan nan a kananan hukumomin Mangu, Bokkos da Barikin Ladi.
Karanta wannan: Gwamnatin jihar Kebbi ta kori wasu hakimai 3 bisa zargin rashin da’a
Eyibio wanda kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya wakilta ya ce, “Ranar Alhamis da misalin karfe 10 na dare aka tsegunta mana game da wasu da ke shirin kai hari a yankin Ntam da kuma ASTC da ke Karamar Hukumar Mangu.
“Shi ne zaratan jami’anmu suka kai samame suka dakile yunkurin kai harin” Inji shi.
Ya kara da cewa, “Jami’anmu sun dakile yunkurin masu kona gidaje da wuraren ibada a yankin Panyam da taimakon wasu dattawan yankin.“











































