Gwamnatin tarayya ta gargadi masu zanga-zanga kan lalata ababen more rayuwa

protesters in Abuja

Gwamnatin tarayya ta bayyana goyon bayanta ga ‘yancin ‘yan kasa musamman matasa na yin zanga-zanga, tare da amincewa da koke-kokensu da kuma muhimmancin fadin albarkacin bakinsu.

Sai dai gwamnatin ta yi gargadi kan duk wani nau’i na lalata ababen more rayuwa yayin zanga-zangar, tare da jaddada bukatar gudanar da zanga-zangar lumana.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin Ministan Cigaban Matasa, Kwamared Ayodele Olawande, a Abuja ranar Litinin, yayin da yake amsa tambayoyi daga jaridar Vanguard.

Olawande ya bayyana cewa, yayin da gwamnati ta amince da sahihancin batutuwan da masu zanga-zangar suka gabatar, yana da matukar muhimmanci a ci gaba da gudanar da zanga-zangar cikin lumana ba wai ta rikide zuwa tashin hankali ko lalata dukiyoyin jama’a ba.

Karanta: Yan sanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye kan masu zanga-zanga a Abuja

Da yake bayyana goyon bayansa ga ‘yancin gudanar da zanga-zangar, Olawande ma ya bayyana cewa, da ya samu lokaci, da da kansa zai shiga zanga-zangar.

Ya ce, “Kowa na da ‘yancin yin zanga-zanga, a gaskiya idan na samu lokaci, zan shiga zanga-zangar da kaina, akwai ‘yancin fadin albarkacin baki ga kowa.

Matasan da ke zanga-zangar suna da kwararan dalilai sun ga wasu batutuwa kuma suna jin cewa akwai bukatar su yi magana, shi ya sa suke fitowa kan tituna.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here