Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Kogi, Wemi Jones, ya ce gwamnatin jihar ba ta da wani shiri na korar wani malamai.
Kwamishinan ya yi wannan karin haske ne a wata sanarwa da ya fitar a yau Juma’a a Lokoja, yayin da ya ke mayar da martani kan rahotannin da ke yawo a wasu sassan kafafen yada labarai na cewa “Gwamna Yahaya Bello ya bayar da umarnin korar malaman Kogi wadanda ba sa goyon bayan APC.”
Kwamishinan ya bayyana rahoton da ake yadawa a matsayin “labarai na karya, cikakken sharri, kazafi, kuma maras tushe”.
“Wannan hasashe ne na wasu marasa kishin kasa da ke yin kamfen din adawa da nufin haifar da rashin jituwa a tsakanin malamai da ma’aikata a jihar.
“A gaskiya ma, gwamnatin jihar na shirin fitar da jerin sunayen mutane 1,500 da suka yi nasara a ka ɗauke su aiki a matsayin malamai a makarantun sakandire na jihar a matakin farko na shirin daukar malamai.
“Don haka, rahoton da ake yaɗawa ƙarya ce ziryan,” in ji shi













































