Kotun daukaka kara ta Abuja, reshen Abuja, ta gama sauraron karar da bangaren gwamnan Kano Abdullahi Ganduje na jam’iyyar APC a Kano ya shigar yana kalubalantar bangaren Sanata Ibrahim Shekarau.
A ranar Juma’a ne dai kotun ta saurari bayanai daga bangaren masu kara da wanda ake kara.
Solacebase ta ruwaito cewa kotun ta ce za a sanar da ranar da za a yanke hukunci ga bangarorin.
Muna tafe da cikakken bayani nan gaba.












































