Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya naɗa tsohon mai taimaka masa kan harkokin kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad, a matsayin babban mai taimaka masa na musamman kan sadarwar zamani.
kamfanin dillancin labarai na
kasa (NAN) ya rawaitu cewa Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, shi ne ya tabbatar da naɗin da wata takardar ɗaukar aiki da ya aike wa Bashir Ahmad, ranar 20 ga watan Yuli.
A takardar wacce NAN ta ci karo da ita ranar Lahadi a Abuja, Mustapha ya ce naɗin ya fara aiki ne daga ranar 19 ga watan Yulu, 2022.













































