Buhari ya nemi Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Kwamishinonin NMDPRA

65CA2D1C C28A 4FFC A3E0 E4C042D0F7E9
65CA2D1C C28A 4FFC A3E0 E4C042D0F7E9

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aikewa da Majalisar dattijai neman bukatar  tabbatar da mutane biyar da aka nada a matsayin manyan daraktocin hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya (NMDPRA).

Bukatar na kunshe ne a cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Janairu 31, kuma shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya karanta a zauren majalisar ranar Laraba.

Wadanda aka nada a cewar Buhari sun hada da: Francis Alabo Ogaree, Babban Darakta a masana’antar sarrafa carbon, ginawa da ababen more rayuwa da sufuri da Dr. Mustapha Lamorde, babban darakta a fannin lafiya, tsaro, muhalli da al’umma.

Sauran sun hada da Mansur Kuliya, Babban Darakta a Asusun Kayayyakin Gas na Midstream da Downstream, Bashir Sadiq, Babban Darakta a Sabis na  Gudanarwa da Dokta Zainab Gobir, Babban Darakta, Dokokin Tattalin Arziki da Tsare-tsare.

Buhari ya bukaci a gaggauta tabbatar da sunayen wadanda aka nada, domin basu damar fara aiki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here