Hukumar Zabe ta sa ranar da za a gudanar da zaben cike gurabi a Kano, Gombe da wasu jihohi 2

INEC Chairman Joash Amupitan

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sa ranar 19 ga Satumba domin gudanar da zaben cike gurabi 5 a jihohin Najeriya 4 da suka hada da Gombe, Kano, Bauchi da Delta.

Sakataren Yada Labara Shugaban INEC, Mr. Tunde Oketola, ne ya bayyana hakan a cikin hirar da ya yi da kamfanin dillacin labarai na kasa (NAN) a ranar Talata a Abuja.

Oketola ya ce zaben cike gurabin ya kunshi na dan majalisar tarayya 1 da majalisun dokoki jihohi 4.

A cewar Oketola, za a gudanar da zaben cike gurabin a Mazabar Gombe, Kwami da Funakaye a Jihar Gombe.
Na mazabun jihohi kuma sun hada da: Mazabar Disina da Sakwa a Jihar Bauchi, Udu a Jihar Delta da Dawakin Kudu a Jihar Kano
(NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here