Hukumar Gudanarwa ta KHAIRUN ta ziyarci Sarkin Dutse, tana neman goyon baya ga ci gaban jami’ar

IMG 20260903 WA0561 750x430

Hukumar gudanarwar Jami’ar Khalifa Isyaku Rabiu da ke Kano (KHAIRUN), karkashin jagorancin Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdulrashid Garba, ta kai wata ziyarar ban girma ga Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hameem Nuhu Sanusi, a fadarsa da ke Dutse, Jihar Jigawa.

A cewar jami’ar, ziyarar wadda aka gudanar a ranar Alhamis, na da nufin karfafa dangantaka tsakanin Jami’ar da Masarautar Dutse, tare da neman albarka, jagoranci da goyon bayan sarkin domin ci gaba da bunkasa ta.

Yayin da yake jawabi a lokacin ziyarar, Farfesa Garba ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya ba da damar gudanar da wannan ziyara da aka dade ana shiryawa, inda ya bayyana ta a matsayin wata muhimmiyar dama ta kawo KHAIRUN kusa da masarautar a hukumance tare da neman shawara da albarkar Sarki.

SolaceBase ta ruwaito cewa, Shugaban Jami’ar ya kuma jaddada tarihi da ci gaban KHAIRUN, yana mai cewa jami’ar tana ci gaba da janyo hankalin dalibai daga sassan shiyyar, ciki har da Jihar Jigawa.

A cewarsa, kusan dalibai 100 daga Jihar Jigawa ne a halin yanzu suke karatu a KHAIRUN, inda wasu ke amfana da tallafin karatu (scholarships), yayin da wasu kuma iyayensu ke daukar nauyinsu.

Farfesa Garba ya tabbatar wa Sarkin kudirin jami’ar na ba da gagarumar gudunmawa ga ci gaban ilimi a shiyyar, sannan ya nuna godiyarsa bisa lokacin da aka ware wa tawagar tasa.

Da yake jawabi, Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hameem Nuhu Sanusi, ya yi maraba da tawagar KHAIRUN tare da nuna farin cikinsa da wannan ziyara.

Sarkin ya amince cewa ziyarar ta zo a makare ba lokacin da aka tsammata ba, amma ya ce ya fahimci dimbin ayyukan da ke gaban Shugaban Jami’ar, saboda haka, ya yaba wa hukumar gudanarwar jami’ar bisa kokarin da suka yi na ziyartar masarautar.

Ya bayyana KHAIRUN a matsayin tasu, Sarkin ya tabbatar wa jami’ar cikakken goyon bayansa, yana mai jaddada cewa jami’ar tana wakiltar wani muhimmin sashe na kyawawan ayyukan da marigayi Khalifa Isyaku Rabiu ya bari.

Ya yi alkawarin cewa Masarautar Dutse za ta yi duk abin da za ta iya don tallafa wa jami’ar da kuma ba da gudunmawa ga ci gaba da samun nasararta.

Sarkin ya kuma bayyana irin abubuwan da suka faru tsakaninsa da marigayi Khalifa Isyaku Rabiu, musamman zuwansa gidan marigayi Sheikh domin karatun Alkur’ani.

Ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayi Khalifa, ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya ci gaba da sanya albarka ga abubuwan da ya bari, sannan ya ba KHAIRUN dorewar ci gaba, nasara da tasiri mai kyau ga al’umma.

Jami’ar ta kara da cewa wannan ziyara ta nuna wani muhimmin mataki na karfafa alaka tsakanin KHAIRUN da Masarautar Dutse, kuma tana tabbatar da hadin gwiwar da ke tsakaninsu wajen samar da ilimi, ci gaban al’umma da kuma adana ayyukan alkhairi na marigayi Khalifa Isyaku Rabiu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here