PSG ta ci gaba da rike kambun Kofin Zakarun Turai bayan doke Arsenal

AFP 20260530 B4HK8P9 v1 MidRes FblEurC1PsgArsenalFinal 750x430

Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain (PSG) ta ci gaba da rike kambunta a gasar cin kofin zakarun Turai ta UEFA a ranar Asabar bayan ta doke Arsenal da ci 4-3 a bugun daga kai sai mai tsaran-gida a wasan karshe mai cike da daure kai wanda aka tashi 1-1 bayan karin lokaci a birnin Budapest.

Kai Havertz ne ya fara sa Arsenal a gaba a minti na 6, amma bugun daga kai sai mai tsaran-gidan da Ousmane Dembele ya ci bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne ya baiwa PSG sabuwar dama, wacce daga karshe ta yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaran-gida ta ci gaba da rike kofin Turai da ta lashe a bara.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here