Zamba a Intanet: EFCC ta kama wasu ‘yan kasar China 4, da wasu karin mutane 101  

Chinese EFCC

Hukumar Yaki da Yiwa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC), ta kama mutane 105 da suka hada da ‘yan kasar China hudu, a wani rukunin kasuwanci da ke unguwar Gudu a Abuja bisa zargin zamba ta intanet.

Kakakin ta, Dele Oyewale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja

Ya ce an kama su ne a wani samame da jami’an hukumar suka yi.
Oyewale ya ce kama wani bangare ne na kokarin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ke yi na tsaftace al’ummar kasar daga damfarar intanet da sauran ayyukan cin hanci da rashawa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here