Tinubu Ya Isa Birnin Guinea-Bissau.

Tinubu arrives Guinea Bissau 750x430

Shugaba Bola Tinubu, a karshen mako a Guinea-Bissau, ya ce Najeriya ta kuduri aniyar kiyaye zaman lafiya da tabbatar da dorewar dimokuradiyya a yammacin Afirka.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan ayyuka na musamman, sadarwa Dele Alake, ya fitar a karshen mako.

Shugaba Tinubu ya ce Najeriya za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na sa ido wajen karfafa dimokradiyya kamar yadda ta yi a kasashen Laberiya da Saliyo.

“Najeriya kasa ce da ta yi fice a Saliyo da Laberiya da sauran wurare,” in ji shi.

Ya godewa sojojin da kwamandan su, Janar Al-Hassan Grema, bisa sadaukarwa da hidimar da suke yi wa Najeriya da kuma kasar da ta karbi bakuncinsu.

A nasa bangaren, Birgediya Janar Grema ya bayyana jin dadin sojojin ga Shugaba Tinubu kasancewarsa babban kwamandan na farko a tarihin Najeriya da ya ziyarci sojojinsa a kasashen waje.

Tun da farko, jirgin shugaban ya sauka a filin jirgin sama na kasa da kasa da ke birnin Bissau da misalin karfe 5:30 na yamma agogon kasar gabanin taron kungiyar ECOWAS, wanda shi ne karon farko da ya shiga kasar Afrika ta kudu tun bayan hawansa karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ana sa ran shugabannin yankuna 16 da ke halartar taron za su yi shawarwari kan batutuwa biyar masu muhimmanci a yankin.

Sauran batutuwan da za a yi la’akari da su sun hada da rahoton halin da ake ciki a Jamhuriyar Mali, Burkina Faso da Guinea, da takardar sheda kan shirin bai wa kungiyar ECOWAS kudin bai daya da kuma rahoton cikas ga ‘yancin zirga-zirgar kayayyaki a kan hanyar Abidjan zuwa Legas.

Sanarwar ta kara da cewa ana sa ran shugaba Tinubu zai dawo Najeriya ranar Litinin mai zuwa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here