
Shugaban kasa, Bola Tinubu ya biya wasu kudade da kungiyar Super Eagles da sauran kungiyoyin wasannin kasar nan, ke bin gwamnatin tarayya.
A wata sanarwa da aka fitar a shafin X na cibiyar yada labaran Tinubu, a ranar Lahadi, ta ce biyan bashin ya hada da bashin albashin manyan masu horaswa na tawagar har na tsawon watanni 15, da kuma alawus-alawus ‘yan wasa mata, da kuma ‘yan kasa-kasa da shekaru 20 na tawagar kasa.
Karanta wannan: Tsohon dan wasan Super Eagles Justice Christopher ya rasu
Sanarwar ta ci gaba da cewa, shugaban kasa ya amince da biyan Naira biliyan 12 na baya-bayan nan ga kungiyoyin Najeriya na wasanni daban-daban, wadanda suka hada da Super Eagles da sauran su.
muna tafe da karin bayani………..












































