A ranar Juma’a ne wasu gwamnoni hudu suka isa harabar kotun koli domin fara zaman kotu.
Gwamnonin sun hada da Bala Mohammed na jihar Bauchi da Abba Kabir Yusuf na jihar Kano da Caleb Mutfwang na jihar Filato da kuma Dauda Lawal na Zamfara.
Karanta wannan: Mai Magana da yawun gwamnan jihar Borno Isah Gusau ya mutu
Ana sa ran kotun za ta yanke hukunci kan takaddamar zaben gwamna a jihohi takwas, da suka hadar da Legas da Filato da Bauchi da kuma Kano.
Karanta wannan: Za’a rantsar da sabbin alkalan kotun koli guda 11
Sai jihohin Abia da Ebonyi da Zamfara da kuma jihar Cross River.
Muna tafe da Karin bayani….