Gobara ta kone ofishin hukumar zabe a Ibadan

Fire marlet 1

Hukumar zabe mai zaman kanta INEC reshen jihar Oyo ta tabbatar da tashin gobara a ofishin hukumar  na karamar hukumar Ibadan ta kudu maso gabas.

A wata sanarwa da kwamishinan zaben jihar Dakta Adeniran Tella, ya fitar da yammacin Juma’a yace gobarar ta tashi ne da misalin karfe 10 da mintuna 30 na safe.

Karanta wannan: Yanzu-yanzu:Ganduje ya nemi Abba Gida-gida ya koma APC

Sanarwar tace har kawo lokacin rubuta wannan labari ba a gano musabbabinta ba.

A ranar Asabar 3 ga watan Fabrairu mai kamawa ne hukumar ta INEC zata gudanar da zabukan cike gurbi tare da sake wasu a jihohin kasar nan 9.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here