Shugabannin kungiyar kwadago na tare hanyoyin shiga da fita filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.
Shugabannin kungiyar kwadagon sun ce zanga-zangar na zuwa ne bisa umarnin hedikwatarta ta kasa kan cin zarafin da aka yiwa shugaban NLC, Joe Ajaero a jihar Imo.
Mambobin kungiyoyin kwadago na kasar nan NLC da TUC sun tare hanyoyin shiga da fita filin jirgin ne da safiyar ranar Alhamis 9 ga watan da muke ciki na Nuwamba, inda matafiya da dama suka makale.

















































