Jam’iyyar PDP ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, domin sasanta ‘ya’yan jam’iyyar da ke korafi gabanin taron majalisar zartarwa ta kasa.
An bayyana hakan ne a karshen taron da shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya gudanar a masaukin Abuja a daren Lahadi.
Taron ya kuma samu halartar Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike. Sai dai bai yi magana da manema labarai ba.
Labari mai alaƙa: Cikin Hotuna: Wike, Gwamnonin PDP, da sauran su sun hadu domin tattauna rikicin shugabancin jam’iyyar
Wasu daga cikin gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Ademola Adeleke (Osun), Caleb Mutfwang (Plateau), Ahmadu Fintiri (Adamawa), Seyi Makinde (Oyo), da Peter Mbah (Enugu).
Sauran sun hada da tsoffin gwamnonin Cross River, Liyel Imoke, Achike Udenwa na Imo, Olagunsoye Oyinlola na Osun, Okezie Ikpeazu na Abia, da Seriake Dickson na Bayelsa.
Shugaban riko na jam’iyyar PDP na kasa, Umar Damagun, tsohon shugaban kwamitin riko, Ahmed Markafi, da wasu mambobin kwamitin ayyuka na jam’iyyar na kasa su ma sun halarci taron.
Da yake zantawa da manema labarai, gwamnan Bauchi ya ce an gudanar da taron ne a daidai lokacin da jam’iyyar ke kokarin gudanar da taron NEC, wanda aka shirya gudanarwa a karshen watan Mayu.
A cewarsa, gayyatar da tsaffin gwamnonin suka yi masa, an yi shi ne domin sanin abubuwan da suka faru da su, ta yadda za su iya magance wasu matsalolin cikin gida da kuma shirya fage na gudanar da taron NEC ba tare da matsala ba, da kuma babban taron kasa nan gaba a shekara.
Da aka tambaye shi game da sauya shekar ‘ya’yan jam’iyyar PDP na baya-bayan nan, gwamnan jihar Bauchi ya ce, hakan ci gaban ne kuma zai kara musu karfi.
Sai dai ya bayyana cewa jam’iyyar na tsara dabarun ganin an kwato wasu daga cikin jihohin da jam’iyyar ke da gwamnoni.
An dai nuna damuwa kan sauya sheka da gwamnan jihar Delta Sheriff Oborevwori da majalisarsa suka yi zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Jam’iyyar adawa dai na fama da rikice-rikicen cikin gida tun bayan babban zaben shekarar 2023.
Lamarin ya kara ta’azzara sakamakon rikicin da ya barke tsakanin tsohon gwamnan jihar Rivers da magajinsa, Sim Fubara.
Kokarin da shugabannin jam’iyyar suka yi, da suka hada da kwamitin ayyuka na kasa, kwamitin amintattu, kwamitin zartarwa na kasa, da kungiyar gwamnonin PDP, na sasantawa, bai kawo karshen rikicin ba.
A ranar 23 ga Afrilu, Oborevwori, tsohon gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, da wasu jami’an jihar sun koma APC.
A majalisar dokokin jihar Kebbi, ‘yan majalisar wakilai uku, Sanata Adamu Aliero (Kebbi ta tsakiya), Sanata Yahaya Abdullahi (Kebbi ta Arewa), da Garba Maidoki (Kebbi ta Kudu), sun shiga jam’iyya mai mulki bayan wata ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu.
Da yawa daga cikin jiga-jigan ‘yan adawa na ganin ci gaban a matsayin wani shiri ne na mayar da kasar mai jam’iyya daya.













































