A karshe, APC ta sanar da INEC cewa za ta gudanar da babban taron kasa ranar 26 ga watan Fabrairu

D40F6D69 3CD1 4141 8C2D E799DC721FEE
D40F6D69 3CD1 4141 8C2D E799DC721FEE

A karshe Shugabancin riko na jam’iyyar APC karkashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni ya rubutawa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC takarda, inda ta sanar da ita babban taronta na kasa da za ta gudanar a ranar 26 ga watan Fabrairu.

An dai yi ta rade-radin cewa wasu ‘yan siyasa a cikin jam’iyyar na shirin sauya ranae babban taron.

Sai dai a cikin wasikar mai dauke da kwanan watan 2 ga watan Fabrairu mai dauke da sa hannun Gwamna Mai Mala Buni da Sakatare, Sanata John James Akpanudoedehe, jam’iyyar ta ce za ta gudanar da babban taronta na kasa a ranar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here