a safiyar yau alhamis Shugaban kasa Muhammadu Buhari isa jihar Legas domin kaddamar da wasu ayyuka, tare da halartar taron kaddamar da littafin tarihin rayuwar Bisi Akande tsohon Shugaban riko na jam’iyyar APC
Wata sanarwa da aka fitar ta bayyana cewa cikin ayyukan da shugaba Buhari zai kaddamar akwai wasu sabbin jiragen ruwa na yaki a tashar sojojin ruwa dake Victoria Island a cikin garin Legas.
Rahotanni sun bayyana cewa tun a safiyar yau alhamis jami’an tsaro wanda suka hada sojoji da ƴan sanda da jami’an DSS suka mamaye unguwar Victoria Island wanda nan ne shugaban zai je.













































