Zaɓen 2023: Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa ta bada Umarnin rufe Jami’o’i

National Universities Commision NUC
National Universities Commision NUC

Hukumar kula da jami’o’i ta kasa ta bayar da umarnin rufe jami’o’in kasar nan domin baiwa dalibai damar shiga zaben shekarar da muke ciki ta 2023.

A wata wasika da hukumar ta NUC ta aikewa shugabannin jami’o’i da daraktocin cibiyoyi na jami’o’i, NUC ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan umarnin ministan ilimi Adamu Adamu.

A ranar 25 ga watan nan da muke ciki na Fabrairu ne za’a fara gudanar da babban zaɓen kasar nan.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here