Yanzu-yanzu: Gwamna Yusuf ya mika sunan Shehu Sagagi, Dahiru Hashim, da wasu mutane 4 ga majalisar dokokin jihar a matsayin wadan da zai nada kwamishinoni

Abba Kabir Yusuf 1 750x430.jpeg

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya mika sunayen mutane 6 ga majalisar dokokin jihar a matsayin kwamishinoni.

Kakakin majalisar, Ismail Jibrin Falgore ne ya sanar da hakan a ranar Litinin yayin da yake karanta wasikar gwamnan a zauren majalisar.

SolaceBase ta rahoto cewa wadanda aka nada sun hada da, Shehu wada Sagagi, Dr Dahiru Mohd Hashim, Ibrahim Abdullahi Wayya, Dr Isma’il Dan Maraya,  Gaddafi Sani Shehu da  Abdulkadir AbdulSalam.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here