Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin ƙaramin ministan kuɗi.
An gudanar da bikin rantsarwar ne a taƙaice a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Litinin.
Tun da fari jami’an tsaro na fadar shugaban ƙasa sun tantance Oyedele tare da matarsa da misalin ƙarfe 2:09 na rana, inda sabon ministan ya sanya rigar kwat mai launin shuɗi mai duhu, yayin da matarsa ta sanya kayan gargajiya masu launin fari.













































