Ina Neman Afuwar Musulmai Bisa Furucin Da Na Yi Kan Zaben Majalisar Dattawa — Kashim Shettima

0

Maitamakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya ce yana neman afuwar al’ummar Musulmi bisa wasu kalamai da ya yi game da zaben shugabannin Majalisar Dokokin Tarayya.

A cewar Mataimakin Shugaban Kasar, ba a fahimci maganar a muhallinta ba, kuma ba shi da wata manufa na bata sunan addininsa.

Sanata Kashim a tattaunawarsa da BBC ya ce ya yi wadannan kalamai ne saboda maslahar Najeriya, ganin cewa suna da wasu bayanan sirri da bai dace ya fito bainar jama’a yana bayani a kansu ba.

Sannan yadda lamura ke tafiya a Najeriya a wannan lokaci, dole shugabanni su fito su ja hankali domin wanzuwar kasar baki-daya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here