Ina Neman Afuwar Musulmai Bisa Furucin Da Na Yi Kan Zaben Majalisar Dattawa — Kashim Shettima

Kashim Shettima
Kashim Shettima

Maitamakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya ce yana neman afuwar al’ummar Musulmi bisa wasu kalamai da ya yi game da zaben shugabannin Majalisar Dokokin Tarayya.

A cewar Mataimakin Shugaban Kasar, ba a fahimci maganar a muhallinta ba, kuma ba shi da wata manufa na bata sunan addininsa.

Sanata Kashim a tattaunawarsa da BBC ya ce ya yi wadannan kalamai ne saboda maslahar Najeriya, ganin cewa suna da wasu bayanan sirri da bai dace ya fito bainar jama’a yana bayani a kansu ba.

Sannan yadda lamura ke tafiya a Najeriya a wannan lokaci, dole shugabanni su fito su ja hankali domin wanzuwar kasar baki-daya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here