El-Rufai ya gana da Aregbesola, Tunde Bakare gabanin zaben 2027

elrufai 666x430

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ziyarci tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, da limamin coci Fasto Tunde Bakare a Legas.

Mai baiwa El-Rufai shawara kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye ne ya bayyana ziyarar a cikin wani sakon Twitter a ranar Lahadi.

Ganawar El-Rufai da manyan mutane biyu na zuwa ne kwanaki kadan bayan ziyarar da ya kai wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a Kaduna.

Karin karatu: Tinubu ne yaƙi amincewa da naɗi na a matsayin minista, ba majalisar dattawa ba – El-Rufai
Kasancewar sa a Legas ya haifar da sabon cece-ku-ce game da makomar siyasarsa da kuma dabarun kawancen da zai yi gabanin zaben 2027.

Aregbesola, wanda tsohon gwamnan jihar Osun ne a karo na biyu, ya fice daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a kwanakin baya bayan da aka dade ana rikicin cikin gida a jam’iyyar reshen jihar Osun.

Shi kuwa Bakare na cikin shahararrun muryar siyasa kuma tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here